Shugaban Ghana, John Mahama, ya sadaukar da sabuwar sarautar gargajiya da aka ba shi, Aare Atayeto Oodua of the Source, ga Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a Ile-Ife, Jihar Osun.
An ba Mahama sarautar ne daga Ooni na Ife, Oba Adeyeye Ogunwusi, a wani biki da ya nuna al’adun gargajiya da zumuncin da ke tsakanin al’ummar Ghana da Najeriya.
Mahama ya ce, “Sadaukarwar tana nuna dankon zumunci, girmamawa da haɗin kai tsakanin yan Afirka.”
Ya jaddada cewa al’ummar yankin na da tarihi da asali iri ɗaya, kuma ya kamata su ci gaba da gina gadar fahimta da zumunci a Afirka ta Yamma.
Ooni na Ife ya ce, “Dangantakar Ghana da Najeriya tana nuna cewa Afirka iyali ɗaya ce, yana mai cewa iyakokin da aka ƙirƙira bai kamata su raba al’ummar Afirka ba.”
Taron ya gudana ne a matsayin wani bangare na bukukuwan cika shekaru 10 na nadin sarautar Ooni na Ife.
