Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai ta Najeriya, Benjamin Kalu, ya ce lokaci ya yi da ECOWAS ta daina “hadin gwiwar takardu” ta koma hadin gwiwar aiki wajen aiwatar da yarjejeniyar AfCFTA.
Ya bayyana hakan a taron majalisar da aka yi a Abuja, yana mai nuna cewa ko da yake cinikayyar cikin Afirka ta kai dala biliyan 220.3 (16%) a 2025, cinikayya a cikin ECOWAS ta tsaya a 11.5%, duk da damar kasuwa mai kimanin dala tiriliyan 3.4.
Kalu ya ce, matsalolin hanya da tsaiko a iyakoki na kara jinkirta ci gaba. Ya jaddada cewa korido na Abidjan–Lagos babban ginshikin tattalin arzikin yanki ne, amma har yanzu ba a kammala shi ba kuma cunkoso da takardun gwamnati su ne manyan kalubale.
A bangaren hada kudade, ya ce tattaunawa kan kudin Eco ta dade amma bai zama mai yiwuwa ba. Ya bada shawarar a mayar da hankali kan PAPSS, wanda ke ba da damar biyan kudi kai tsaye cikin kudaden kasashen yanki ba tare da dogaro da Dalar Amurka ba.
Ya ce wannan tsarin ya fi saurin zama mafita ga yan kasuwa a Najeriya, Cote d’Ivoire da Gambiya, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da ECOWAS ta aiwatar da manufofin da ke aiki kai tsaye maimakon dogon tattaunawa.
